Posts

Da alama za a 𝔇ibi yan kallo domin Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello, ya bayyana cewa zai tsaya takarar kujerar Sanata a Kogi ta Tsakiya a shekarar 2027, kujerar da Sanata Natasha ke rike da ita a yanzu. #LeadershipMatters

𝐘𝐀𝐍 𝐉𝐀𝐑𝐈𝐃𝐀 7 𝐒𝐔𝐍 𝐑𝐀𝐒𝐔 𝐒𝐀𝐊𝐀𝐌𝐀𝐊𝐎𝐍 𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐑𝐈𝐍 𝐌𝐎𝐓𝐀 Labari marar dadin ji da hukumar kiyaye haddura ta kasa reshen jihar 𝐆𝐨𝐦𝐛𝐞 ta tabbatar da rasuwar Ma’aikatan gidan Talabijin na NTA 7 a Jihar Gombe, sun rasa rayukansu ne sakamakon hatsarin mota da ya rutsa da su a hanyarsu daga Gombe zuwa Yola. Rahotan ya ce ‘yan jarida bakwai sun rasa rayukansu, inda huɗu suka jikkata sakamakon Hatsarin Motar da ya rutsa da su a hanyar Gombe zuwa birnin Yola, jihar Adamawa. Tawagar ƴan jaridan da ke cikin motar Ƙungiyar NUJ reshen jihar Gombe, wanda wasu rahotanni sun ce za su halarci ɗaurin auren wani ɗan jarida ne lamarin ya rutsa da su a hanya. Allah Ya jikansu da rahama, Ya gafarta musu kurakuransu, Ya kuma ba iyalansu, NUJ da NTA, ‘yan uwansu da abokan aiki haƙurin jure wannan babban rashi. Tabbas an sami babban gibi a wannan bangare. #Punch NewsPaper

Rundunar ƴan sandan jihar Kebbi ta tabbatar da faruwar tashin Bam a asibitin ƙwararru na Bagudo da ke jihar. Da yake yiwa manema labarai jawabi kakkakin rundunar ƴan sandan SP Bashir Usman ya ce babu labarin rasa rai kawo yanzu. #rfihausa

DA DUMI-DUMI: Wutar lantarkin Najeriya ta sake lalacewa a yau Litinin. Shin ko kuna da wutar NEPA yanzu haka a inda kuke? Abba Pantami

Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Abdulkadir Mohammed, ya bada umarnin gyara Makarantar Firamaren garin Tafare da kuma wutar lantarki ga al’ummar garinda ke Karamar Hukumar Alkaleri. Gwamnan ya ba da wannan umarni ne lokacin da al’ummar Tafare suka tsayar da tawagar motocinsa gwamnan a hanyarsa ta zuwa Alkaleri daga garin Duguri inda suka koka kan tsawon lokaci da suka shafe ba tare da wutar lantarki ba, da kuma lalacewar ginin makarantar firamare guda ɗaya dake Garin. Gwamna Bala Mohammed ya kewaya don duba halin da makarantar ke ciki, tare da nuna damuwa kan mummunan yanayin da ake koyarwa, inda ya umarci ma’aikatar da abin ya shafa da su fara aikin gyara nan take, tare da gina ƙarin azuzuwa domin rage cunkoso. Haka kuma, ya umarci hukumomin da suka dace da su gaggauta dawo da wutar lantarki ga al’ummar Tafaren.

'𝐘𝐚𝐧 𝐁𝐚𝐧𝐠𝐚 𝐚 𝐤𝐚𝐫𝐚𝐦𝐚𝐫 𝐡𝐮𝐤𝐮𝐦𝐚𝐫 𝐀𝐥𝐤𝐚𝐥𝐞 𝐧𝐚 𝐜𝐢𝐤𝐢𝐧 𝐀𝐥𝐤𝐡𝐚𝐢𝐫𝐢. Yayin da Gwamnan Jihar Bauchi Sen. Bala Abdulkadir Mohammed ya miƙa musu baburan hawa.

Kakakin Rundunar Sojin Saman Najeriya, Ehimen Ejodame, ya ce dakarun rundunar sun yi nasarar kai farmaki mabuyar 'yan ta'adda a tsaunin Turba da sansanin Kachalla Dogo Sule a jihar Zamfara.

Comrade Sabo Muhammad ya bayar da gudummawar Dalar Amurka ɗari ($100) domin sayen kujerun zama a Makarantar Sakandaren Jibril Aminu da ke Bauchi, da nufin inganta yanayin koyarwa da koyo a makarantar. Ya sanar da tallafin ne a yayin taron cika shekaru goma (2015–2025) da kammala karatu a makarantar, wani biki da Ƙungiyar Tsofaffin Daliban Makarantar Sakandaren Jibril Aminu ta shirya a Bauchi. Comrade Sabo Muhammad ya bayyana cewa gudummawar na daga cikin ƙoƙarinsa na tallafa wa ci gaban ilimi da kuma Mara wa Gwamnati baya wajan karfafa ilimi. Shugabannin makarantar da ƙungiyar tsofaffin daliban sun nuna jin daɗinsu bisa wannan tallafi, tare da yin alƙawarin amfani da kuɗin yadda ya dace domin amfanin ɗalibai da bunƙasa harkokin ilimi a makarantar.

Gwamnatin Tarayya ta kafe cewa sai an fara aiwatar da sabbin dokokin gyaran haraji a ranar 1 ga Janairu, 2026, tana mai cewa gyare-gyaren an yi su ne da nufin farfado da tattalin arziki da kuma wadata ga 'yan Najeriya.

KAI TSAYE: Daga gidan gwamnatin jihar Bauchi wajen gaisuwar bikin kirsimeti da mabiya addinin Kirista ke kawowa gwamnan jihar Bauchi.

DA DUMI DUMI: Uwar Gidan Gwamnan Jihar Bauchi Hajiya Aisha Bala Mohamed Ta Sauke Press Sakatariyar Ta Murjanatu Musa Maidawa Daga Mukaminta Wannan Sanarwar Yafito ne Daga Offishin Uwar Gidan Gwamnan Jihar Bauchi (OFFICE OF THE FIRST LADY BAUCHI).

Ba na tunanin akwai 'yan ta'addar kungiyar ISIS a jihar Sokoto, inda Donald Trump ya ce ya kai hari in ji masanin tsaro, Dr. Audu Bulama Bukarti. Sai dai Dr. Bulama ya ce idan har shugaban na Amurka ya yi nasarar samun 'yan bindiga irinsu Lakurawa da ke yankin Sokoto da Kebbi, to hakan zai zama babbar nasara a yakin da ake yi da 'yan bindiga.

Yanzu-yanzu: Jirgin United Nigeria Airline ya isa tashar Murtala Muhammad dake Legas, domin daukar fasinjan Kano da su ka shafe sama da awanni 3 suna jira. Hotuna daga Muhammad Alfanda.

HALIN DA AKE CIKI A GARIN JABO JIHAR SOKOTO Bayan harin da Amerika ta kaddamar a garin Jabo, an sake gano wani abu mai kama da abin fashewa a wani wuri daban, daga inda na farko ya fado zuwa wannan wurin, kimanin rabin kilomita ne Lokacin da aka fara tono wurin, an hango wani karfe mai kama da abin da ya fashe jiya, sai aka bada shawarar a dakatar da tonon, domin ana kyautata zaton cewa watakila abu ne mai fashewa da bai tashi ba Saboda haka, muna kira ga dukkan al’umma da su guji kusantar wannan wuri, kada su yi kokarin dubawa ko tana komai, su bar wurin gaba daya har sai an tabbatar da jami'an tsaro da suke da fasahar wannan aikin sun ciresa Muna rokon Allah Ya kare 'yan uwanmu, Allah Ya mayar wa Ameirka sharri da makircinta wa Musulmi

Wannan ne karon farko da Amurkan ke kai hari Najeriya da sunan yaƙi da ta'addanci tun bayan da Donald Trump ya yi barazanar ɗaukar matakin Soji kan ƙasar game da zargin kisan Kiristoci, sai dai wasu ganau daga jihar Sokoto sun ce harin na Amurka ya faru ne a yankin da bashi da tarihin faruwar hare-haren ƴan bindiga kuma ya shafi tarin fararen hular da basu ji ba basu gani ba. Ƙarin bayani: https://rfi.my/CIWD.f

Kawo yanzu babu wata ƙungiya da ta ɗauki alhakin kai wannan harin, da ake kyautata zaton na ƙunar baƙin wake ne. Ƙarin bayani - https://bbc.in/3KPHYRH

Rundunar ‘yan sandan Jihar Borno ta tabbatar da samun wani lamari da ake zargin tashin bam ne a Masallacin Jumu'a na Al-Adum da ke Kasuwar Gamboru a birnin Maiduguri.

Yayin da Hanyar sama da gwamnan Bauchi keyi saura kiris ta kammala. shin zaku iya bayyana yawan hanyoyin da Kauran Daulan Usmaniya 𝑺𝒂𝒏𝒂𝒕𝒂 𝑩𝒂𝒍𝒂 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒌𝒂𝒅𝒊𝒓 𝑴𝒖𝒉𝒂𝒎𝒏𝒂𝒅 yayi a karamar hukumar ku?

Hotuna: Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf a yanzu haka yana kaddamar da jami'an tsaron unguwanni da za su yi aikin samar da tsaro a faɗin jihar. Rahotanni sun bayyana cewa, za a baiwa jami'an damar rike bindigogi da alburusai inda za su yi aiki a kananan hukumomi 44 na jihar Kano. 📸 Bashir Ahmad (X)

#HOTUNA: Yadda Gwamnan Filato, Caleb Mutfwang, ya kaddamar da dakarun sabuwar hukumar tsaro ta jihar mai sunan ‘Rainbow’ mutum 1400. 📸: Leadership Hausa

Shin Yaya yanayin tafiye tafiye na karshen shekara, kun tafi hutu ko kuna shirin zuwa hutun? Ku bayyana Mana ra'ayoyinku domin mu karanta muku a cikin shirinmu na Rumfa Sha Shirgi.