Posts

Showing posts from December 30, 2025

Da alama za a 𝔇ibi yan kallo domin Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello, ya bayyana cewa zai tsaya takarar kujerar Sanata a Kogi ta Tsakiya a shekarar 2027, kujerar da Sanata Natasha ke rike da ita a yanzu. #LeadershipMatters

π˜π€π π‰π€π‘πˆπƒπ€ 7 𝐒𝐔𝐍 𝐑𝐀𝐒𝐔 π’π€πŠπ€πŒπ€πŠπŽπ π‡π€π“π’π€π‘πˆπ πŒπŽπ“π€ Labari marar dadin ji da hukumar kiyaye haddura ta kasa reshen jihar π†π¨π¦π›πž ta tabbatar da rasuwar Ma’aikatan gidan Talabijin na NTA 7 a Jihar Gombe, sun rasa rayukansu ne sakamakon hatsarin mota da ya rutsa da su a hanyarsu daga Gombe zuwa Yola. Rahotan ya ce ‘yan jarida bakwai sun rasa rayukansu, inda huΙ—u suka jikkata sakamakon Hatsarin Motar da ya rutsa da su a hanyar Gombe zuwa birnin Yola, jihar Adamawa. Tawagar Ζ΄an jaridan da ke cikin motar Ƙungiyar NUJ reshen jihar Gombe, wanda wasu rahotanni sun ce za su halarci Ι—aurin auren wani Ι—an jarida ne lamarin ya rutsa da su a hanya. Allah Ya jikansu da rahama, Ya gafarta musu kurakuransu, Ya kuma ba iyalansu, NUJ da NTA, ‘yan uwansu da abokan aiki haΖ™urin jure wannan babban rashi. Tabbas an sami babban gibi a wannan bangare. #Punch NewsPaper

Rundunar Ζ΄an sandan jihar Kebbi ta tabbatar da faruwar tashin Bam a asibitin Ζ™wararru na Bagudo da ke jihar. Da yake yiwa manema labarai jawabi kakkakin rundunar Ζ΄an sandan SP Bashir Usman ya ce babu labarin rasa rai kawo yanzu. #rfihausa