Nishadi Radio international
Posts
Posted by
Nishadi Radio international
Ba na tunanin akwai 'yan ta'addar kungiyar ISIS a jihar Sokoto, inda Donald Trump ya ce ya kai hari in ji masanin tsaro, Dr. Audu Bulama Bukarti. Sai dai Dr. Bulama ya ce idan har shugaban na Amurka ya yi nasarar samun 'yan bindiga irinsu Lakurawa da ke yankin Sokoto da Kebbi, to hakan zai zama babbar nasara a yakin da ake yi da 'yan bindiga.
Posted by
Nishadi Radio international
HALIN DA AKE CIKI A GARIN JABO JIHAR SOKOTO Bayan harin da Amerika ta kaddamar a garin Jabo, an sake gano wani abu mai kama da abin fashewa a wani wuri daban, daga inda na farko ya fado zuwa wannan wurin, kimanin rabin kilomita ne Lokacin da aka fara tono wurin, an hango wani karfe mai kama da abin da ya fashe jiya, sai aka bada shawarar a dakatar da tonon, domin ana kyautata zaton cewa watakila abu ne mai fashewa da bai tashi ba Saboda haka, muna kira ga dukkan al’umma da su guji kusantar wannan wuri, kada su yi kokarin dubawa ko tana komai, su bar wurin gaba daya har sai an tabbatar da jami'an tsaro da suke da fasahar wannan aikin sun ciresa Muna rokon Allah Ya kare 'yan uwanmu, Allah Ya mayar wa Ameirka sharri da makircinta wa Musulmi
Posted by
Nishadi Radio international
Wannan ne karon farko da Amurkan ke kai hari Najeriya da sunan yaƙi da ta'addanci tun bayan da Donald Trump ya yi barazanar ɗaukar matakin Soji kan ƙasar game da zargin kisan Kiristoci, sai dai wasu ganau daga jihar Sokoto sun ce harin na Amurka ya faru ne a yankin da bashi da tarihin faruwar hare-haren ƴan bindiga kuma ya shafi tarin fararen hular da basu ji ba basu gani ba. Ƙarin bayani: https://rfi.my/CIWD.f
Posted by
Nishadi Radio international
Hotuna: Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf a yanzu haka yana kaddamar da jami'an tsaron unguwanni da za su yi aikin samar da tsaro a faɗin jihar. Rahotanni sun bayyana cewa, za a baiwa jami'an damar rike bindigogi da alburusai inda za su yi aiki a kananan hukumomi 44 na jihar Kano. 📸 Bashir Ahmad (X)
Posted by
Nishadi Radio international
Morocco ta faro gasar lashe kofin nahiyar Afrika da ƙafar dama, bayan da ta samu nasara kan Comoros da ci 2 da nema. Ɗan wasan gaba na tawagar Morocco Brahim Diaz ne ya fara jefa kwallo a raga a minti na 55, kafin Ayoub El Kaabi da ya shigo ya ƙara a minti na 74. 📸/Reuters
Posted by
Nishadi Radio international













