Posts

Kawo yanzu babu wata ƙungiya da ta ɗauki alhakin kai wannan harin, da ake kyautata zaton na ƙunar baƙin wake ne. Ƙarin bayani - https://bbc.in/3KPHYRH

Rundunar ‘yan sandan Jihar Borno ta tabbatar da samun wani lamari da ake zargin tashin bam ne a Masallacin Jumu'a na Al-Adum da ke Kasuwar Gamboru a birnin Maiduguri.

Yayin da Hanyar sama da gwamnan Bauchi keyi saura kiris ta kammala. shin zaku iya bayyana yawan hanyoyin da Kauran Daulan Usmaniya 𝑺𝒂𝒏𝒂𝒕𝒂 𝑩𝒂𝒍𝒂 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒌𝒂𝒅𝒊𝒓 𝑴𝒖𝒉𝒂𝒎𝒏𝒂𝒅 yayi a karamar hukumar ku?

Hotuna: Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf a yanzu haka yana kaddamar da jami'an tsaron unguwanni da za su yi aikin samar da tsaro a faɗin jihar. Rahotanni sun bayyana cewa, za a baiwa jami'an damar rike bindigogi da alburusai inda za su yi aiki a kananan hukumomi 44 na jihar Kano. 📸 Bashir Ahmad (X)

#HOTUNA: Yadda Gwamnan Filato, Caleb Mutfwang, ya kaddamar da dakarun sabuwar hukumar tsaro ta jihar mai sunan ‘Rainbow’ mutum 1400. 📸: Leadership Hausa

Shin Yaya yanayin tafiye tafiye na karshen shekara, kun tafi hutu ko kuna shirin zuwa hutun? Ku bayyana Mana ra'ayoyinku domin mu karanta muku a cikin shirinmu na Rumfa Sha Shirgi.

Gwamnatin Najeriya ta ayyana Thursday 25 ga Disamba da Friday 26 ga Disamba, 2025 a matsayin ranakun hutun Kirisimeti da Boxing Day, tare da kuma Alhamis 1 ga Janairu, 2026 domin bikin Sabuwar Shekara.

MRS: An Sauke Farashin Man Fetur a Jihohin Najeriya, Lita Ta Koma Ƙasa da N740 0 An wallafa 22 Dis 2025 da ƙarfe 4:49 Yamma Daga Sani Hamza wanda ya yi bita Muhammad Malumfashi 3 - tsawon

Tankar Man fetur makare da fetur ta Kama Da Wuta A Gidan Man Alh. Hamzat Ahmad Talban Dass Dake Karamar Hukumar Dass. Allah ubangiji ya kiyaye na gaba. Hoto: #AbdurrazaqYChinko

Morocco ta faro gasar lashe kofin nahiyar Afrika da ƙafar dama, bayan da ta samu nasara kan Comoros da ci 2 da nema. Ɗan wasan gaba na tawagar Morocco Brahim Diaz ne ya fara jefa kwallo a raga a minti na 55, kafin Ayoub El Kaabi da ya shigo ya ƙara a minti na 74. 📸/Reuters

Iyalan marigayi Sheikh Dahiru Bauchi sun bayyana yadda mutane miliyan 63 suka amfana da ilmin da Allah ya ba shi -

An Buɗe HINSAD General Hospital a Bauchi, An Fara Duba Marasa Lafiya 1,000 Kyauta An buɗe wani sabon asibiti mai zaman kansa mai suna HINSAD General Hospital Ltd a garin Bauchi, Jihar Bauchi, domin ƙara inganta harkokin kiwon lafiya da rage raɗaɗin jinya ga al’umma. Bayan buɗe asibitin, shugabannin HINSAD General Hospital sun sanar da fara duba marasa lafiya guda 1,000 (dubu ɗaya) kyauta, a matsayin gudummawa ga lafiyar jama’a da kuma tallafa wa marasa galihu.

Kamannin Amarya Sun Canza Bayan Ɗaurin Aure..

Daga Kannywood

Jam'iyyar PDP reshen Jihar Jigawa ta yi Allah-wadai da dakatarwar da Kwamitin Amintattu na jam’iyyar ya yi wa tsohon gwamna kuma dattijo a jam'iyyar, Alhaji Sule Lamido, inda suka buƙaci a janye dakatarwar nan take.Jam’iyyar ta ce dakatarwar ba ta da tushe, kuma ba ta dace da ka’idoji da dokokin jam’iyyar ba, tana mai jaddada cewa Sule Lamido jigo ne kuma dattijo wanda ya bayar da gudummawa mai yawa ga jam'iyyar tun kafuwarta.