Majalisar Koli Kan Harkokin Shari'a ta Najeriya (NJC) ta ce za ta gudanar da bincike kan batutuwan da suka shafi takardun hukuncin zaɓen gwamnan Kano da kotun ɗaukaka ƙara da ke Abuja ta yi.
Majalisar Koli Kan Harkokin Shari'a ta Najeriya (NJC) ta ce za ta gudanar da bincike kan batutuwan da suka shafi takardun hukuncin zaɓen gwamnan Kano da kotun ɗaukaka ƙara da ke Abuja ta yi.
Jaridar Daily Trust a Najeriya ta ambato wasu jami'an majalisar shari'ar ƙasar, na bayyana haka a lokacin da suka ziyarci ofishinta da ke Abuja.
An dai samu ruɗani kan takardun hukuncin shari'ar da kotun ɗaukaka ƙarar ta yi ranar 17 ga watan Nuwamba a shari'a tsakanin gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf, da Nasiru Yusuf Gawuna na APC.

